BANGARAN TAFSIRI

Amsa: Suratul Fatiha da kuma Tafsirinta.
{Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai 1. Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin talikai 2. Mai Rahama Mai Jin ƙai 3. Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako 4. Kai kaɗai muke bautawa, kuma Ka kaɗai muke neman taimakonKa 5. Ka shiryar da mu hanya madaidaiciya 6. Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi akan su ba, kuma ba ɓatattu ba 7}. [Fatiha: 1-7].
FASSARA:

An ambaceta Suratul Fatiha ne؛ domin buɗe littafin Allah da ita.
1- {Da sunan Allah mai yawan rahama ma yawan jinƙai 1.} Ma'ana: Da sunan Allah nake fara karatun Al-ƙur'ani, ina mai neman taimako da shi - maɗaukakin sarki - ina mai neman albarka da ambaton sunan sa.
{Allah}. Wato: Abin bautawa da gaskiya, kuma ba'a ambaton wanin sa da shi - tsarki ya tabbatar masa.
{Ar-Rahman}. Wato: Ma'abocin yalwatacciyar rahama, wacce rahamar sa ta yalwaci dukkan komai.
Arrahim.Mai keɓantacciyar rahama ga muminai kaɗai.
2- {Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai}. Wato: Dukkanin nau'ukan yabo da cika sun tabbata ga Allah shi kaɗai.
3. {Mai yawan rahama mai yawan jin ƙai}. Wato: Mai yalwatacciyar rahama, wacce ta yalwaci kowanne abu, kuma ma'abocin rahama mai saduwa ga muminai.
4. {Mamallakin ranar sakamako}. Itace ranar Al-ƙiyama.
5. {Kai kaɗai muke bautawa kuma gareka kaɗai muke neman taimako}. Wato: Muna bauta maka kai kaɗai kuma muna neman taimako da kai kai kaɗai.
6. {Ka shiryar da mu hanya madaidaiciya}. Itace shiriya zuwa Musulunci da kuma Sunnah.
7. {Hanyar waɗanda ka yi ni'ima agaresu , ba waɗanda ka yi fushi da su ba, ba kuma ɓatattu ba 7}. Wato: Tafarkin bayin Allah na gari daga Annabawa da waɗanda suka biyo su, ba hanyar Nasara da Yahudu ba.
-An sunnanta bayan karanta ta yace (AMIN) wato: Ka amsa mana.

Amsa: Suratul Zalzala da kuma Tafsirinta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
{Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta 1. Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi 2. Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta 3?. A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta 4. Da cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta 5. A rãnar nan mutane zasu fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu 6. To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi 7. Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi 8. [Surat Al-Zilzilah; 1 - 8].
FASSARA:

1- {Idan aka girgiza ƙasa girgizawar nan tata}. Idan aka motsa ƙasa motsawa mai tsanani wanda zai faru gare ta a ranar Al-ƙiyama.
2- {Kuma ƙasa ta fitar da naunye nauyen nan na ta 2}: Kasa ta fitar da duk abinda yake cikinta na matattu da waninsu.
3. {Kuma mutum ya ce me ya sa me ta 3}. Mutum yana mai ɗimaucewa sai ya ce: Wanne al'amari ƙasa take ciki tana motsawa kuma tana bugawa?
4. A wannan ranar za ta ba da labarinta 4}: Acikin wannan yinin mai girman ƙasa za ta bada labari da abinda aka aikata akanta na alkhairi ko na sharri.
5. {Saboda Ubangikinka ya yi mata wahayi 5}: Domin cewa Allah Ya sanar da ita kuma Ya umarce ta da hakan.
6. {Awannan ranar mutane za su fito daban daban domin a nuna musu ayyukansu 6}. A wannan yini mai girman ne wanda ƙasa take girgiza acikinsa, mutane za su fito daga matsayar hisabi a rarrabe؛ domin su ga ayyukan su da suka aikata su a nan duniya.
7. {Wanda ya aikata nauyin komayya na alheri zai gan shi 7}: Wanda ya aikata nauyin ƙaramar tururuwa na ayyukan alheri da biyayya zai gan shi a gabansa.
8. {Wanda ya aikata nauyin komayyana na sharri zai gan shi 8}: Haka kuma duk wanda ya aikata nauyinta na ayyukan sharri zai gan shi a gaban sa.

Amsa: Suratul Adiyat da kuma fassararta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Ina rantsuwa da dawakai masu gudu suna fitar da kukan ciki 1. 2. Masu ƙyasta wuta ƙyastawa 2. 3. Sannan masu kai hari a loakcin Asuba 3. 4.Sai su motsar da ƙũra game da shi 4. 5. Sai su shiga, game da ita (ƙurar) a tsaknin jama'ar maƙiya 5. 6. Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijin sa 6. 7. Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifin sa akan haka 7. 8. Kuma lallai ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne 8. 9. Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin ƙaburbura 9. 10.Aka bayyana abin da ke cikin zukata 10. 11. Lalle ne Ubangijin su, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne? [Surat Al-Adiyat: 1 - 11].
FASSARA:

1. {Ina rantsuwa da dawakai masu gudu suna fitar da kukan ciki 1}: Allah Ya rantse da dawakai masu gudu har ake jin kukan cikin su saboda matsanancin gudu.
2. {Masu ƙyasta wuta ƙyastawa}: Kuma Allah ya rantse da dawakai waɗanda suke ƙyastawa da kofatansu idan suka taka duwatsu, saboda tsananin takawar akan su.
3. {Masu kai hari da Asuba 3}: Kuma Allah ya rantse da dawakai waɗanda suke kai hari ga abokan gaba a lokacin Asuba.
4. {Sai su motsar da ƙura game da shi 4}: Sai su motsar da ƙura saboda gudun su.
5. {Sai su shiga, game da ita a tsakanin jama'a maƙiya 5}: Sai su shiga tsakiya da sadaukan su gaba ɗaya daga maƙiya.
6. {Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa 6}: Lallai mutum mai hanawane ga alherin da Ubangijin sa Ya ke nufin sa daga gare su.
7. {Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifin sa da haka 7}: Lallai cewa shi mai shaida ne akan hanawar sa ga alheri. kuma ba zai taɓa musun haka ba saboda bayyanar sa.
8.{Kuma lalle ne shi ga dukiya shi mai tsananin so ne 8}: Lallai cewa shi saboda tsananin son sa ga dukiya yana rowa da ita ne.
9. {Shin, ba ya sanin cewa idan aka tone abin da yake cikin ƙaburbura 9}: Shin yanzu wannan mutumin mai ruɗuwa da rayuwar duniya idan Allah Ya tayar da waɗanda ke cikin ƙabarbura na matattu, kuma ya fito da su zuwa doran ƙasa domin hisabi da sakamako, to lalle al'amarin bai kasance kamar yanda yake tsammani ba?!
10. {Aka bayyana abinda ke cikin zukata 10}: Kuma aka futo, aka bayyanar da abinda yake cikin zukata na niyyoyi, da ƙudurce-ƙudirce da wasun su.
11. {Lalle ne Ubanginsu game da su a ranar nan, mai ƙididdiga ne 11}: Wato lalle Ubangijinsu dangane da su a wannan ranar wanda zai ba su labari ne, babu wani abinda yake ɓoyuwa a gare shi na al'amarin bayin sa, kuma zai yi musu sakayya akan hakan.

Amsa: Suratul Qari'ah da kuma fassararta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Mai ƙwanƙwasa 1. 2.Mece ce mai ƙwanƙwasar 2? 3. Kuma wane ne ya sanar da kai abin da ake nufi da Maƙwanƙwashiya 3? 4. Rãnar da mutãne za su kasance kamar 'ya'yan fari mãsu wãtsuwa 4. 5.Kuma duwãtsu su kasance kamar gãshin sũfin da aka saɓe 5. 6. To, amma wanda ma'aunansa suka yi nauyi 6. 7. Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda 7. 8. Kuma amma wanda ma'aunansa suka yi sauƙi (bãbu nauyi) 8. 9. To uwarsa Hawiya ce 9. 10 Kuma me ya sanar da kai mece ce ita 10? 11. Wata wuta ce mai zafi 11}. [Surat Al-Qari'ah: 1 - 11].
FASSARA:

1- {Mai ƙwanƙwasa 1}. Al-ƙiyama tana ƙwanƙwasa akan zukatan mutane saboda girman tashin hankalinta.
2. {Mece ce mai ƙwanƙwasa 2}: Mece ce wannan Al-ƙiyamar wacce take ƙwanƙwasar zukatan mutane saboda girman tashin hankalinta?!.
3. {Kuma me ya sanar da kai mecece mai ƙwanƙwasa 3}: Mene ne ya sanar da kai - ya kai wannan Manzo - mecece wannan Al-ƙiyamar wacce take ƙwanƙwasar zukatan mutane, saboda girman sha'aninta, lalle itace ranar Al-ƙiyama.
4. {Ranar da mutane zasu kasance kamar 'ya'yana fari masu watsuwa 4}: Ranar da zata ƙwanƙwashi zukatan mutane su kasance kamar fari masu yaɗuwa masu tarwatsewa nan da can.
5. {Kuma duwatsu su kasance kamar gashin sufin da aka saɓe}: Duwatsu su kasance kamar gashin sufi wanda aka saɓe, acikin sakin tafiyar su da motsin su.
6. {To, amma wanda ma'aunan sa suka yi nauyi 6}: Amma wanda kyawawan ayyukan sa suka rinjayi munanan ayyukan sa.
7. {To, shi yana cikin wata rayuwa yardadda 7}: Shi yana cikin rayuwa yardadda da zai sameta a cikin Aljanna.
8. {To, amma duk wanda ma'aunansa suka yi sauƙi 8}: Amma wanda munanan ayyukansa suka rinjayi kyawawan ayyukansa.
9. {To, Uwar sa Hawiyace 9}: Masaukin sa da madabbatar sa a ranar Al-ƙiyama ita ce Jahannama.
10. {Kuma me ya sanar da kai menene ita 10}: Me ya sanar da kai - ya kai wannan Manzo - mecece ita?!
11. {Wata wuta ce mai zafi}: Ita wuta ce mai tsananin zafi.

Amsa: Suratut Takatur da fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Alfahari da yawan dukiya da dangi ya shagaltar da ku 1. .2. Har kuka ziyarci maƙabartu 2. 3. A'aha! (Nan gaba) zã ku sani 3. 4.A'aha! dai (Nan gaba) zã ku sani 4. 5. Haƙĩƙa, da kuna da sani sani na yaƙĩni 5. 6.Lalle ne zakuga Jahim 6. 7. Sannan kuma lalle ne za ku ganta da idanu, bayyane 7. 8. Sannan lalle ne za a tambaye ku, a rãnar nan lãbãrin ni'imar (da aka yi muku) 8. [Surat At-Takasur: 1 - 8].
FASSARA:

1. {Alfahari da yawan dukiya da dangi ya shagaltar da ku 1}: Alfahari da dukiya da kuma 'ya'ya sun shagaltar da ku - yaku mutane - daga bin Allah.
.2. {Har kuka ziyarci maƙabartu 2}: Har kuka mutu kuka shiga ƙaburburan ku.
3. {A'aha! (Nan gaba) zã ku sani 3}: Abinda yakasance tare da ku har alfahari ya shagaltar da ku daga ƙin bin Allah, to da sannu za ku san ƙarshen wannan shagaltarwar.
4. {A'aha! dai (Nan gaba) zã ku sani 4}: Sannan za ku san ƙarshensa.
5. {Haƙĩƙa, da kuna da sani sani na yaƙĩni}:Tabbas da a ce ku kuna sani na haƙiƙanin cewa lalle ku za'a tasheku a gaban Allah, kuma zai saka muku akan ayyukan ku, da ba ku shagaltu da alfahari da dukiya da kuma 'ya'yaba.
6. {Lalle ne zaku ga Jahim 6}: Kuma wallahi sai kunga wuta a ranar Al-ƙiyama.
7. {Sannan kuma lalle ne za ku ganta da idanu, bayyane 7}:Sannan tabbas zaku ganta gani na haƙiƙa da babu kokwanto acikin sa.
8. (Sannan lalle ne za a tambaye ku, a rãnar nan lãbãrin ni'imar (da aka yi muku) 8}: Sannan kuma tabbas sai Allah ya tambaye ku a kan hakan a ranar akan abin da yayi muku na ni'ima kamar lafiya da wadata da wasunsu.

Amsa: Suratul Asr da kuma fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Ina rantsuwa da zamani 1. 2. Lalle ne mutum yana a cikin hasara 2. 3.Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma sukai wasiyya da gaskiya kuma sukai wasiyya da yin haƙuri 3. [Suratul Asr: 1 - 3].
FASSARA:

1. {Ina rantsuwa da zamani 1}
Allah - tsarki ya tabbatar masa - ya yi rantsuwa da zamani.
2. (Lalle ne mutum yana a cikin hasara 2}: Wato: Dukkanin mutum yana cikin tawaya da kuma halaka.
3. {Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma sukai wasiyya da gaskiya kuma sukai wasiyya da yin haƙuri 3}: Sai dai wanda ya yi imani kuma ya yi aiki na ƙwarai, tare da haka suka yi kira zuwa ga gaskiya, kuma suka yi haƙuri akansa, to waɗannan sune waɗanda suka tsira daga hasara.

Amsa: Suratul Humaza da kuma fassararta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa) 1. 2. Wanda ya tara dũkiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa 2. 3. Yana zaton cẽwa dũkiyarsa za ta dawwamar da shi 3. 4. A'aha! Lalle ne zã a jẽfa shi a cikin Huɗama 4. 5. Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Huɗama 5? 6. Wutar Allah ce wadda ake hurawa 6. 7. Wadda take lẽƙãwa a kan zukata 7. 8. Lalle ne ita abar kullẽwa ce a kansu 8. 9. A cikin wasu ginshiƙai mĩƙaƙƙu 9}. [Surat Al-Humazah: 1 - 9].
FASSARA:

1. Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa) 1}: Azaba da tsananin azaba ta tabbata ga dukkan wanda yake yin gulmar mutane da suka acikin su.
2. {Wanda ya tara dũkiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa 2}: Wanda shi himmar sa ita ce tara dukiya da lissafa ta, ba shi da wata himma in ba haka ba.
2. {Yana zatan cewa dukiyarsa zata dawwamar dashi 3}: Yana zatan cewa dukiyar sa wacce ya tarata zata tseratar da shi daga mutuwa, zai wanzu yana madawwami acikin rayuwar duniya.
4. (A'aha! Lalle ne zã a jẽfa shi a cikin Huɗama 4}: Al'amarin ba kamar yadda wannan jahilin yake hasashe ba ne, tabbas sai an watsa shi a wutar Jahannama wacce take niƙe ta karya duk abinda aka watsa a cikinta saboda tsananin masifar ta.
5. Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Huɗama?Me ya sanar da kai - Ya kai wannan Manzo mai girma- mece ce wannan wutar wacce take haɗe duk abin da aka watsa cikinta?!
6. {Wutar Allah ce wadda ake hurawa 6}: Lallai cewa ita wutar Allah ce abar rurawa.
7. {Wadda take lẽƙãwa a kan zukata 7}: Wacce take zarcewa daga cikin jikkunan mutane zuwa zuciyoyin su.
8. {Lalle ne ita abar kullẽwa ce a kansu 8}: Ita abar kullewace akan waɗanda ake azabtarwa acikin ta.
9. {A cikin wasu ginshiƙai mĩƙaƙƙu 9}: Da wasu turaku miƙaƙƙu dogaye ta yadda bazasu iya fita daga gare ta ba.

Amsa- Suratul Fil da kuma fassararta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba 1? 2. Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba 2? 3. Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a 3. 4. Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta 4. 5. Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye 5. [Surat Al-Fil: 1 - 5].
FASSARA:

1. {Ashe, ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ga mutanen giwa ba 1?}
Ashe ba ka sani ba - ya kai wannan Manzo - yadda Ubangijin ka Ya yi da Abraha ba, shi da mutanan sa ma'abota giwaye,yayin da suka yi nufin rushe Ka'aba?
2. {Ashe, bai sanya kaidinsu a cikin ɓata ba 2?} Haƙiƙa Allah ya mayar da mummunan makircinsu na ruishe Ka'abah acikin tozarta, basu sami abinda sukayi buri na kawar da mutane daga Ka'aba, kuma ba su sami komai daga gare ta ba.
3. {Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a 3}: Kuma ya aika musu da tsuntsaye suka je musu jama'a jama'a.
4. {Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta 4}: Suna jifansu da duwatsu na taɓo masu tsananin zafi.
5. {Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye 5}: Sai Allah Ya mayar da su kamar ganyan karmami da dabbobi suka cinye shi kuma suka take shi.

Amsa: Suratu Kuraishi da fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Saboda sabon Kuraishawa 1. 2. Sabonsu na tafiyar hunturu da ta bazara 2. 3. Sabõda haka sai su bauta wa Ubangijin wannan Gida (Ka'abah) 3. 4. Wanda Ya ciyar da su (Ya hana su) daga yunwa, kuma Ya amintar da su daga wani tsõro 4. [Surat Kuraish: 1 - 4].
FASSARA:

1. {Sabon da Kuraishawa sukayi 1}: Abin nufi da wannan shine abinda suka kasance suna sabo da shi daga tafiya acikin hunturu da bazara.
2. {Sabonsu na tafiyar hunturu da ta bazara 2}: Tafiyar hunturu zuwa Yaman, da tafiyar bazara zuwa ƙasar Sham suna amintattu.
3. {Sabõda haka sai su bauta wa Ubangijin wannan Gida (Ka'abah) 3}: Sai su bautawa Ubangijin wannan ɗakin mai alfarma shi kaɗai, wanda ya sawwaƙe musu wannan tafiya, kada su haɗa shi da kowa wurin bauta.
4. {Wanda Ya ciyar da su (Ya hana su) daga yunwa, kuma Ya amintar da su daga wani tsõro 4}: Shi ne wanda Ya ciyar da su daga yunwa, kuma Ya amintar da su daga tsoro, na abin da Ya sanya azukatan Larabawa na girmama wannan Harami, da girmama mazauna wurin.

Amsa: Suratul Ma'un da kuma fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Shin, ka ga wanda ke ƙaryatãwa game da sakamako 1? 2. To, wannan shi ne ke tunkuɗe marãya (daga haƙƙinsa) 2. 3. "Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci 3. 4. To, bone ya tabbata ga masu yin salla 4. 5. Waɗanda sune masu shagala daga sallar su 5. 6. Waɗanda sune suke yin riya (ga ayyukan su) 6. 7. Kuma suna hana taimako 7}. [Surat Al-Ma'un: 1 - 7].
FASSARA:

1. {Shin, ka ga wanda ke ƙaryatãwa game da sakamako 1?}: Shin kasan wanda yake ƙaryata sakamako a ranar Al-ƙiyama?!
2. {To, wannan shi ne ke tunkuɗe marãya (daga haƙƙinsa) 2.To shi ne wannan wanda ya ke tunkuɗe maraya da ƙarfin gaske daga barin buƙatun sa.
3. {Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci 3}: Ba ya kwaɗaitar da kansa ba kuma ya kwaɗaitar da waninsa akan ciyar da mabuƙaci.
4. {To, bone ya tabbata ga masu yin sallah 4}: Hallaka da azaba sun tabbata aga masu sallah.
5. {Waɗanda suke masu shagala daga sallarsu 5}: Waɗanda sune dangane da sallar su suna wasa da ita ba sa damuwa da ita har lokacinta ya fita.
6. {Waɗanda suke yin riya (ga ayyukansu) 6}: Wato su ne waɗanda suke nuna sallar su da ayyukansu, ba sa yin aiki domin Allah.
7. {Kuma suna hana taimako 7}: Suna hana taimakon wasu a abin da babu wata cutarwa a taimakon da shi.

Amsa: Suratul Kausar da kuma fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
{Lalle ne Mu, Mun baka alheri mai yawa 1. 2. Saboda haka, ka yi salla dõmin Ubangijinka, kuma ka sõke (baiko, wato sukar raƙumi) 2. 3. Lalle mai aibanta ka shi ne mai yankakkiyar albarka 3}. [Surat Al-kausar: 1 - 3].
FASSARA:

1. {Lallai ne mu munbaka alheri mai yawa 1}: Lallai mu munzo maka - ya kai wannan Manzo - da alheri mai yawa, daga cikinsa akwai ƙoramar Al-kausara acikin Aljanna.
2. {Saboda haka, ka yi salla dõmin Ubangijinka, kuma ka sõke (baiko, wato sukar raƙumi) 2}: Sai ka bada godiyar Allah akan wannan ni'ima, ta hanyar yin sallah saboda shi kaɗai, kuma ka yi yanka, saɓanin abin da mushurukai suke aikata shi na neman kusanci ga gumakan su da yankan.
3. {Lalle mai aibanta ka shi ne mai yankakkiyar albarka 3}: Lalle mai ƙinka to shi ne abin yankewa daga dukkanin alheri, abin mantawa wanda in za'a ambace shi za'a ambace shi ne da mummuna.

Amsa: Suratul Kafirun da fassararta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Ka ce: "Ya kũ kãfirai 1. "Bã zan bautã wa abin da kuke bautã wa ba 2 Kuma kũ, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bautã wa ba 3. Kuma nĩ ban zama mai bautã wa abin da kuka bautã wa ba 4. {Kuma kũ, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bautã wa ba 5. Addininku na garẽ ku, kuma addinina yanã gare ni 6}. [Surat Al-Kafirun: 1 - 6].
FASSARA:

1. Ka ce: {Ya kũ kãfirai 1} Ka ce -Ya kai wannan Manzo -Ya ku waɗanda suka kafirce wa Allah.
2. {Bã zan bautã wa abin da kuke bautã wa ba 2}: Ba zan taɓa bautawa duka abinda kuke bautawa ba na gumaka, a yanzu ko a nan gaba.
3. {Kuma kũ, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bautã wa ba 3}: Haka kuma ba za ku zamo masu bauta wa abin da ni na ke bautawa ba, wanda yake shi ne Allah shi kaɗai.
4. {Kuma nĩ ban zama mai bautã wa abin da kuka bautã wa ba 4}: Ni kuma ba zan bautawa abinda kuka bauta wa na gumaka ba.
5. {Kuma kũ, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bautã wa ba 5}: Haka kuma ba za ku zamo masu bauta wa abin da ni nake bautawa ba, wanda yake shi ne Allah shi kaɗai.
6.{Addininku na garẽ ku, kuma addinina yanã gare ni 6}: Addinin ku da kuka ƙirƙira yana gareku, ni kuma addini na wanda Allah ya saukar da shi agare ni yana gare ni.

Amsa Suratul Nasr da kuma fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Idan taimakon Allah ya zo da buɗi 1. 2. Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, jama'a jama'a 2. 3. To, ka yi Tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne 3}. [Surat Al-Nasr; 1 - 3].
FASSARA:

1. {Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara 1} Idan taimakon Allah ya zo wa addinin ka - ya kai wannan manzo - da kuma yadda ya ƙarfafi addinin, kuma buɗe Makkah ya faru.
2. {Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, jama'a jama'a 2}: Kuma ka ga mutane suna shiga addinin musulunci ƙungiya bayan ƙungiya.
3. {To, ka yi Tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne 3}: Ka sani hakan wata alama ce ta kusancin ƙarewar aikin da aka aiko ka da shi, to sai ka yi Tasbihi haɗi da godewa Ubangijinka, domin gode masa a kan wannan ni'ima ta nasara da kuma buɗe Makkah, kuma ka nemi gafarar sa, lalle shi ya kasance mai yawan karɓar tuba ne yana karɓar tuban bayinsa, kuma yana gafarta musu.

Amsa: Suratul Masad da kuma Tafsirin ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Hannãye biyu na Abũlahabi sun taɓe, kuma ya taɓe 1. 2. Dũkiyarsa ba ta tsare masa kõme ba, da abin da ya tãra 2. 3. Zãi shiga wuta mai hũruwa 3. 4. Da kuma matarsa mai ɗaukar iatacen (wuta) 4. 5. A cikin kyakkyãwan wuyanta akwai igiya ta kaba (Rãnar ¡iyãma) 5}. [Surat Al-Masad: 1 - 5].
FASSARA:

1. {Hannãye biyu na Abũlahabi sun taɓe, kuma ya taɓe 1}: Hannayan Abu Lahab sun yi asara, wanda yake kuma shi ne baffan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agareshi - Abu lahab ɗan Abdul muɗallabi, saboda taɓewar aikin sa, domin ya kasance yana cutar da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agareshi -, kuma aikin sa ya taɓe.
2. {Dũkiyarsa ba ta tsare masa kõme ba, da abin da ya tãra 2}: Wane abu ne dukiyar sa da 'ya'yan sa suka tsinana masa? ba su kare shi daga azaba ba, kuma ba su jawo masa rahama ba.
3. {Zãi shiga wuta mai hũruwa}: Zai shiga wata wuta mai huruwa ranar Al-ƙiyama da zai yi fama da zafin ta.
4. {Da kuma matarsa mai ɗaukar iatacen (wuta): Kuma da sannu matar sa Ummu Jamil wacce ta kasance ita ma tana cutar da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ta hanyar zuba ƙaya akan hanyar sa, zata shiga wutar.
5. {A cikin kyakkyãwan wuyanta akwai igiya ta kaba (Rãnar ƙiyãma) 5}: A wuyan ta igiya ce mai ingancin tufkewa za'a koro ta da ita zuwa wuta.

Amsa: Suratul Ikhlas da fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci 1. Allah shi ne abun nufi da bukata 2. 3 Bai haifa ba kuma ba'a haife shi ba 3. 4. Kuma babu ɗaya da ya kasance kini a gare Shi 4}. [Surat Al-Ikhlas: 1 - 4].
FASSARA:

1. {Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci 1} Ka ce: - Ya kai wannan manzo: - Shi ne Allah wanda babu abin bautawa da gaskiya sai shi.
2. {Allah shi ne abun nufi da buƙata 2} Wato: Shi ne wanda ake ɗaga bukatun halittu zuwa gare shi.
3 {Bai haifa ba kuma ba'a haife shi ba 3}: Ba shi da ɗa, tsarki ya tabbata a gare shi, kuma ba shi da uba.
4. {Kuma babu ɗaya da ya kasance kini a gare Shi 4}: Babu kwatankwacin sa a halittar sa.

Suratut Falak da kuma fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
1. {Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya 1. Daga sharrin abin da Ya halitta 2. Daga sharrin dare, idan ya yi duhu 3. Daga sharrin mãtã mãsu tõfi a cikin kuduri 4. Daga sharrin mai hasada idan ya yi hasada 5}. [Surat Al-falaƙ: 1 - 5].
FASSARA:

1. {Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya 1}: Ka ce - Ya kai wannan manzo -: Ina neman kariya daga Ubangijin safiya, ina kuma neman tsarin sa.
2. {Daga sharrin abin da Ya halitta 2}: Daga sharrin abin da zai cuitar daga halittu.
3. {Da sharrin dare, idan ya yi duhu 3}: Ina neman kariya daga Allah daga sharrikan abin da yake bayyana cikin dare na dabbobi da 'yan fashi.
4. {Daga sharrin mãtã mãsu tõfi a cikin kuduri 4}: Ina neman kariya daga gare shi daga sharrin matsafa waɗanda suke tofi a guduri (ƙulli).
5. {Daga sharrin mai hasada idan ya yi hasada 5}: Daga kuma sharrin mai hasada mai ƙiyayya ga mutane, idan yayi musu hassada akan abin da Allah ya ba su na ni'imomin sa, yana son gushewar su daga gare su, da kuma afka cuta da su.

Amsa: Suratul Nas da fassarar ta:
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
{Ka ce: "ina neman tsari ga Ubangijin mutane 1}. Mamallakin mutane 2. Ubangijin Mutane 3. Daga sharrin mai sanya wasuwãsi, mai ɓoyewa 4. Wanda ke sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane 5. Daga Aljannu da mutane 6}. [Suratun Nas: 1 - 6].
FASSARA:

1. {Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin mutane 1}: Ka ce - Ya kai wannan manzo -: Ina neman kariya da Ubangijin mutane, kuma ina neman kulawar sa.
2. {Mamallakin mutane 2}: Wanda Yake tasarriufi acikin su da abin da ya ga dama, ba su da wani mamallaki in ba shi ba.
3. {Ubangijin Mutane 3}: Abin bautar su da gaskiya, babu wani abin bauta gare su da gaskiya in ba shi ba.
4. {Daga sharrin mai sanya wasawasi, mai boyewa 4}: Daga sharrin shaiɗan wanda yake jefa waswasin sa ga mutane.
5. {Wanda yake sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane 5}: Yake jefa wasiwasin sa a zukatan muta ne.
6. {Daga Aljannu da mutane 6}: Wato: Mai jefa wasawasin yana kasancewa daga cikin mutane kuma yana kasancewa daga cikin Aljannu.