BANGAREN ADDU'OI DA ZIKIRI

Amsa: Annabi - tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: Misalin wanda yake ambaton Ubangijin sa, da wanda ba ya ambaton Ubangijin sa, kamar rayayye ne da mataccce". Bukhari ne ya rawaito shi.
- Wannan kenan؛ domin darajar rayuwar mutum (tana tabbata ne) da gwargwadon ambaton sa ga Allah - maɗaukakin sarki -.

Amsa: 1. Yana kawo yardar Mai Rahama.
2. Yana korar Shaiɗan.
3. Yana kare musulmi daga saharruka.
4. Lada da sakamako suna tabbata ta dalilin sa.

Amsa: "Babu abIn bautawa da gaskiya sai Allah". Al-Tirmizi da Ibnu Majah ne suka ruwaito shi.

Amsa: "Dukkan godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya rayar da mu bayan Ya matar da mu, kuma taruwa tana gare Shi". An haɗu akan sa (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

Amsa: "Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya tufatar da ni wannan tufafin kuma ya azurtani shi, ba tare da wata dabara daga gareni ko ƙarfi ba". Abu Daud da Al-Tirmizi ne suka ruwaito shi.

Amsa: "Da sunan Allah". Al-Tirmizi ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Ya Allah, godiya ta tabbata gare Ka, kai ne ka tufatarda ni shi, ina roƙon Ka alherin sa da alherin abinda akayi domin sa, ina kuma neman tsarin Ka daga sharrin sa, da kuma sharin abinda akayi domin sa". Abu Daud da Al-Tirmizi ne suka ruwaito shi.

Amsa: Idan ka ga sabon tufafi ga waninka sai kayi masa addu'a, ka ce: " (Fatan Allah ) yasa ka tsufantar da ita, kuma Allah - maɗaukakin sarki - Ya canza ma ka (wata)". Abu Daud ne ya ruwaito shi.

"Ya Allah lallai ni ina neman tsarin Ka daga shaiɗanu maza da shaiɗanu mata". An haɗu akan sa (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

Amsa: "Ina neman gafarar Ka". Abu Daud da Al-Tirmizine suka ruwaito shi.

Amsa: "Da sunan Allah". Abu Daud da waninsa ne suka ruwaitoshi.

"Ina shida cewa babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kaɗai yake, bashi da abokin tarayya, kuma ina shaida cewa Annabi Muhammad bawan Sa ne kuma Manzon Sa ne". Muslim ne ya rawaito shi.

Amsa: "Da sunan Allah, na dogara ga Allah, babu dabara, babu ƙarfi sai ga Allah". Abu Daud da Al-Tirmizine suka ruwaito shi.

Amsa: "Da sunan Allah muka shiga, da kuma sunan Allah muka fita, kuma ga Allah Ubangijin Mu muka dogara, sannan yayi sallama ga iyalan sa". Abu Daud ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Ya Allah Ka buɗe mini ƙofofin rahamar Ka". Muslim ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Ya Allah ina roƙon Ka daga falalar Ka". Muslim ne ya ruwaito shi.

Amsa: Ina faɗin abinda mai kiran sallar yake faɗa, sai dai a: "Kuyi gaggawa zuwa ga sallah". Da kuma "Kuyi gaggawa zuwa ga tsira". Sai in ce: "Babu dabara kuma babu ƙarfi sai ga Allah". An haɗu akansa (Bukhari da Muslim suka ruwaito shi).

Amsa: "Kana yin sallati ne ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -. Muslim ne ya ruwaito shi. Kuma sai ka ce: "Ya Allah ma'abocin wannan cikakkiyar addu'a, da sallah mai tsayawa, Ka baiwa (Annabi) Muhammad Wasila (Matsayine a Aljanna) da fifiko, Ka tayar da shi wani matsayi abin yabo, wanda Ka yi alƙawarin sa". Bukhari ne ya ruwaito shi.
Sai ka yi addu'a tsakanin kiran sallah da kuma iƙama, domin addu'a (awannan lokacin) ba'a dawo da ita.

Amsa. 1. Ina karanta Ayatul Kursiyyu: {Allah, bãbu wani abin bautawa da gaskiya fãce Shi, Rãyayye, Mai tsayuwa da kõme, gyangyaɗi bã ya kãma Shi, ballantana barci, Shi ne da abin da yake a cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasa. Wane ne wanda yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa? Yana sanin abin da yake a gaba gare su da abin da yake a bãyansu. Kuma bã su kẽwayẽwa da kõme daga ilminSa, fãce da abin da Ya so. KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa. Kuma tsare su bã ya nauyayarSa. Kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma}. [Surat Al-Baƙara: 255]. 2. Ina kuma karanta: Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jin ƙai. 1. {Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci 1. Alla shi ne abun nufi da Buƙata 2. 3 Bai haifa ba kuma ba'a haife shi ba 3. 4. Kuma babu ɗaya da ya kasance kini a gare Shi 4}. Kafa uku. Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. 1. {Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya 1. Daga sharrin abin da Ya halitta 2. Daga sharrin dare, idan ya yi duhu 3. Daga sharrin mãtã mãsu tõfi a cikin kuduri 4. Daga sharrin mai hasada idan ya yi hasada 5}. Kafa uku. Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai. {Ka ce: "ina neman tsari ga Ubangijin mutane 1}. Mamallakin mutane 2. Ubangijin Mutane 3. Daga sharrin mai sanya wasuwãsi, mai ɓoyewa 4. Wanda ke sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane 5. Daga Aljannu da mutane 6}. Kafa uku. 3. "Ya Allah kaine Ubangijina babu abin bautawa da gaskiya sai Kai, Ka halicceni kuma nine bawan Ka, kuma ni ina kan alƙawarin Ka da wuyayen Ka iya iyawata, ina neman tsarin Ka daga sharrin abinda na aikata, ina iƙirari da ni'imar Ka gareni, kuma ina iƙirari da zunubi na, to ka gafarta mi ni, cewa shi ba mai gafarta zunubai sai Kai". Bukhari ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Da sunan Ka ya Allah nake mutuwa kuma nake rayuwa". An haɗu akan sa (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

Amsa: "Da sunan Allah".
To idan ka manta a farko, sai ka ce:
"Da sunan Allah a farkon sa da kuma ƙarshen sa". Abu Daud da Al-Tirmizi ne suka ruwaito shi.

Amsa: "Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya ciyar da ni wannan, kuma ya azurtani shi, ba tare da wata dabara daga gare ni ko ƙarfi ba". Abu Dawud da Ibnu Majah da wasun su ne suka ruwaitoshi.

Amsa: "Ya Allah ka sanya musu albarka a abinda ka azurta su da shi, ka kuma gafarta musu ka yi musu rahama". Muslim ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Godiya ta tabbata ga Allah".
Kuma ɗan'uwan sa ko abokin sa ya ce da shi:
"Allah Ya yi maka rahama".
4. Idan ya faɗa masa: sai ya ce: "Allah Ya shiryar da ku, kuma Ya kyautata sha'aninku". Bukhari ne ya ruwaito shi.

"Tsarki ya tabbatar maKa da godiyar Ka, ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Kai, ina neman gafarar Ka kuma ina tuba zuwa gare Ka". Abu Daud da Tirmizi da wasun su ne suka ruwaito shi.

Amsa: Da sunan Allah, godiya ta tabbata ga Allah. {Tsarki ya tabbata ga wanda Ya hore mana wannan, kuma mu bamu kasance muna da rinjaye gareshiba 14}, "Godiya ta tabbata ga Allah, godiya ta tabbata ga Allah, godiya ta tabbata ga Allah, Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma, tsarki ya tabbata gare Ka, ya Allah lallai ni na zalinci kaina, to Ka gafarta mini, domin babu mai gafarta zunubai sai Kai". Abu Daud da Al-Tirmizi ne suka ruwaito shi.

Amsa: "Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma {Tsarki ya tabbata ga wanda ya hore mana wannan, kuma mu bamu kasance muna da rinjaye gareshiba 14}. Ya Allah lallai muna roƙan Ka a wannan tafiya tamu ayyukan ƙwarai da tsoron Ka, daga aiki kuma wanda Kake yarda (Dashi). Ya Allah Ka sawwaƙe mana wannan tafiya tamu, Ka naɗe mana tsawonta. Ya Allah Kai ne ma'aboci a wannan tafiya, kuma halifan mu a iyalan mu. Ya Allah lallai muna neman tsarin Ka daga wahalhalun tafiya, da kuma mugun gani, da mummunar makoma a dukiya da iyali".
Idan kuma ya dawo sai ya faɗesu, ya kuma ƙara:
"Muna masu dawowa, masu tuba, masu bauta, masu godiya ga Ubangijin mu". Muslim ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Ina bawa Allah ajiyarku wanda abubuwan da aka baShi ajiya basa tozarta". Ahmad da Ibnu Majah ne suka ruwaito shi.

Amsa: "Ina bawa Allah ajiyar addinin ka, da amanar ka, da ƙarshen aikin ka". Ahmad da Tirmizi ne suka ruwaito shi.

Amsa: "Babu abin bautawa da cancanta sai Allah Shi kaɗai yake ba shi da abokin tarayya, mulki nasa ne, kuma godiya tasa ce, Yana rayawa kuma Yana kashewa, Shi ne rayayye wanda ba ya mutuwa, dukkanin alhairai suna hannun Sa, kuma Shi Mai iko ne akan dukkan komai". Al-Tirmizi da Ibnu Majah ne suka ruwaito shi.

"Ina neman tsarin Allah daga Shaiɗan abin jefewa". An haɗu akansa (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi).

Amsa; "Allah Ya saka maka da Alheri". Al-Tirmizi ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Da sunan Allah". Abu Daud ne ya ruwaito shi.

Amsa: "Dukkan godiya ta tabbata ga Allah wanda da ni'amar Sa ne kyawawan ayyuka suke cika". Al-Hakim ne da wani suka ruwaito shi.

Amsa: "Dukkan godiya ta tabbata ga Allah akowane irin hali". Sahihul Jam'i.

Amsa: Mutum musulmi yana cewa: "Amincin da rahamar Allah da kuma albarkar Sa su tabbata a gare ku".
Sai ɗan'uwansa ya mayar masa:
"Ku ma amincin Allah da rahamar Sa da albarkar Sa su tabbata a gareku". A Tirmizi da Abu Dawud da kuma wanin su.

"Ya Allah (ka sanya shi) mamakon ruwa mai amfani". Bukhari ne ya ruwaito shi.

Amsa: "An yi mana ruwa ne da falalar Allah da kuma rahamar Sa". Bukhari da Muslim.

Amsa: "Ya Allah ina roƙon Ka alherin ta, ina kuma neman tsarin Ka daga sharrin ta". Abu Dwud da Ibnu Majah.

Amsa: "Tsarki ya tabbata ga wanda tsawa take tasbihi haɗi da gode maSa, Mal'iku kuma saboda tsoran Sa". Muwaɗɗa Malik.

Amsa: "Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya bani lafiya daga abinda ya jarabe ka da shi, kuma ya fifita ni akan mafi yawan abinda ya halitta fifitawa". Al-Tirmizi ne ya ruwaito shi.

Amsa: (Ya zo) a Hadisi: "Idan ɗayan ku yaga abinda ya ƙayatar da shi daga ɗan'uwan sa, ko karan kan sa, ko a dukiyar sa, to ya yi addu'a ta samun albarka (Allah ya sanya albarka) domin lallai kambun baka gaskiya ne". Ahmad da Ibnu Majah da wasunsu ne suka ruwaito shi.

Amsa: "Ya Allah! Ka yi daɗin tsira ga (Annabi) Muhammad da iyalan (Annabi) Muhammad, kamar yadda Ka yi salati ga (Annabi) Ibrahim da iyalan (Annabi) Ibrahim, lallai Kai abin godewa ne kuma Maigirma. Ya Allah! Ka yi albarka ga (Annabi) Muhammad da iyalan (Annabi) Muhammad kamar yadda Ka yi albarka ga (Annabi) Ibrahim da iyalan (Annabi) Ibrahim, lallai Kai abin godewa ne kuma maigirma". An haɗu akansa (Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi).